in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muhimman labarai daga wasu jaridun Najeriya
2016-06-17 19:40:52 cri
--Yayin da bankunan kasuwancin Najeriya ke shirin daidaitawa da sabon tsarin musayar kudin kasar da na kudaden waje wanda zai fara a ranar Litinin mai zuwa, a yau ne kuma babban bankin kasar wato CBN zai bayyana sunayen dillalan da za su jagoranci tsarin.(Vanguard)

--Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya ce shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya zai dawo gida daga London inda ya kwashe kwanaki 10 yana jinyar ciwon kunnen da ya ke fama da ita ne a ranar Lahadi.

Yemi Osibanjo ya shaidawa wakilan kafofin watsa labarai da ke fadar shugaban kasa hakan ne a jiya Alhamis jim kadan kafin fara taron majalisar tattalin arzikin ta kasa da ya gudana a fadar shugaban kasar da ke Abuja,fadar mulkin Najeriya.(The Punch)

--A jiya ne hukumar EFCC da ke yaki da masu yiwa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa ta damke tsohon shugaban hukumar kwastan na kasar Abdullahi Dikko Inde, bisa zargin da ake masa na almundahanar kudade.(Daily Trust)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China