in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mayakan Boko Haram sun halaka mutane 18 a Najeriya
2016-06-17 21:07:25 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, wasu da ake zaton mayakan Boko Haram ne ,sun kashe mutane 18 a kauyen Kuda-Kaya da ke karamar hukumar Madagali a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin kasar.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Adamawa Othman Abubakar ya shaidawa wakilin kamfanin dillancin labarai na Sin Xinhua da ke Yola, fadar mulkin jihar cewa, harin ya faru ne da misalin karfe 10 na dare agogon wurin.

Kakakin 'yan sanda ya kuma tabbatar da cewa,'yan sanda sun yi nasara damke wani da ake zaton mayakin Boko Haram ne a garin Gombi da ke jihar ta Adamawa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China