in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara aikin gyaran babban filin jiragen sama na kasar Togo
2016-04-25 13:33:21 cri
A ranar 23 ga wata ne, aka kaddamar da bikin bude aikin gyaran babban filin jiragen sama na kasar Togo wato Niamtougou da kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin yinsa. Shugaban kasar Togo da shugaban majalisar dokokin kasar da firaministan kasar, da ministan kula da ababen more rayuwa da zirga-zirga, Ninsao Gnofam da jakadan Sin dake kasar Togo Liu Yuxi da kansula a fannin kasuwanci da sauran wakilan kasashen biyu sun halarci bikin.

Bayan kammala aikin, za a tsawaita hanyar saukar jiragen sama da tsawon mita 500, ta yadda manyan jiragen sama na kasar, za su iya sauka ba tare da matsala ba. Rahotanni na cewa, yawan kudin kwangila ya kai dalar Amurka miliyan 68, kuma za a shafe watanni 12 ana wannan gyara.

A yayin bikin, Ministan Gnofam ya ce, filin jiragen sama na Niamtougou ya kasance wani muhimmin filin jiragen sama dake yankin arewacin kasar Togo, gwamnatin Sin da bankin EXIM na Sin suna daga cikin wadanda suka dauki nauyin wannan aiki, bayan da aka gyara shi, zai kuma kyautata yanayin sufuri da ake ciki a yankin Kara da sauran wurare, da raya tattalin arziki da yawon shakatawa a arewacin kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China