in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tur da harin birnin Orlando na Amurka
2016-06-13 11:07:23 cri
Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon a jiya Lahadi ya yi Allah wadai da kaddamar da kazamin hari a birnin Orlando dake jahar Florida a Amurka, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 50 tun a farkon wannan rana.

Cikin wata sanarwa daga mai magana da yawunsa, Ban ya gabatar da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, sannan ya nuna goyon baya ga gwamnatin Amurka.

Wasu 'yan bindiga ne dai dauke da makamai suka bude wuta a wani wurin shakatawa a Orlando tun a farkon ranar Lahadi, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 50.

Shugaba Barak Obama ya bayyana harin a matsayin hari mafi muni da ya hallaka jama'a a Amurka, inda ya bayyana shi a matsayin aikin 'yan ta'adda.

Wani kamfanin dillanci labaru na Amaq ya bayyana cewar mayakan kungiyar IS ne suka kaddamar da harin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China