in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar harkokin wajen Sin ta yi bayani kan ziyarar da shugaba Xi Jinping a Uzbekistan
2016-06-23 20:30:56 cri
A jiya Laraba ne a cibiyar watsa labaru ta tawagar kasar Sin da ke Tashkent, mai ba da taimako ga ministan harkokin wajen kasar Sin, mista Li Huilai ya yiwa taron manema labaru karin haske game da ziyarar aikin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai a kasar ta Uzbekistan

A yayin taron, Li ya bayyana cewa, ziyarar aikin da shugaba Xi ya kai a Uzbekistan, da halartar taron kolin kungiyar SCO da ya gudana a Tashkent, muhimman ayyukan harkokin waje ne da kasar Sin ta yi a Uzbekistan da yankin tsakiyar Asiya baki daya, wadanda suka jawo hankulan kasashen Sin da Uzbekistan har ma da kasashen duniya kwarai. A cikin sa'o'i fiye da 20, shugaba Xi ya halarci bukukuwa fiye da 10, baya ga yin cudanya da takwaransa na Uzbekistan Islam Karimov, inda suka yi musayar ra'ayoyi kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, hadin kai a tsakaninsu a fannoni daban daban da kuma batutuwan duniya da na shiyya shiyya dake jawo hankulansu, sun kuma cimma ra'ayi daya. Ana iya cewar, an cimma gagarumar nasara a wannan ziyara. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China