in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da harin ta'addanci kan yankin bakin tekun Syria
2016-05-24 10:57:50 cri

Kakakin babban magatakardan MDD Ban Ki-moon, ya fidda wata sanarwa a jiya Litinin, inda ya yi Allah wadai da jerin hare-haren ta'addanci da aka kai wa yankunan arewa maso yammacin kasar Syria wadanda ke bakin teku, ya kuma kalubalanci bangarori daban daban da su martaba yarjejeniyar tsagaita bude wuta domin kare rayukan al'ummar.

Kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya fidda wani labari a jiya Litinin, wanda ke cewa, an kai hare-haren boma-bomai sau da dama a yankunan arewa maso yammacin kasar dake bakin teku, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 65. An kuma ce, kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai hare-haren na biranen Tartous da Jableh.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China