in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An halaka masu gadin shugaban kasa 22 a Libya
2016-05-19 09:44:19 cri
Rahotanni daga kasar Libya na cewa, a kalla masu gadi a ofishin shugaban kasa 22 ne suka gamu da ajalinsu kana wasu 30 suka jikkata bayan da wani bam da aka dana a cikin wata mota ya tashi a lokacin da suke fafatawa da mayakan IS a birnin Sirte na kasar Libya.

Daya daga cikin masu aiki a cibiyar watsa labarai dake gadi ofishin shugaban kasar ta Libya Osama Badi ya shaida wa kamfanin dillancin labaru na kasar Sin Xinhua cewa, wani dan kunar bakin wake ne ya kaiwa masu gadin shugaban kasa a garin Bowerat Al-Hassan da ke kusa da Sirte hari, inda suka kashe masu gadin 18 kana suka jikkata 30, baya ga wasu masu gadin 4 da aka halaka gabanin kai harin bam din.

Wata majiya a babban asibitin Misrata ta tabbatar da cewa, an kai gawawwakin mutane 22, sannan tana jiran karin wasu gawawwakin.

Gwamnatin hada kai ta kasar Libya wadda ke samun goyon bayan MDD, ta kafa rukunin masu gadi a ofishin shugaban kasa ne a kokarin da ake na karya lagon mayakan IS. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China