in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalisar tarayyar Turai ya yi kira ga jama'ar Birtaniya da su nuna goyon baya kan zaman kasarsu a cikin kungiyar EU
2016-06-21 11:17:07 cri
Shugaban majalisar tarayyar Turai Donald Tusk dake ziyara a kasar Portugal ya yi kira ga jama'ar kasar Birtaniya da su jefa kuri'un nuna goyon baya ga Birtaniya da ta cigaba da kasancewa a cikin kungiyar EU.

Tusk ya bayyana a gun taron manema labaru bayan ganawarsa tare da firaminsitan kasar Potugal Antonio Maria Costa cewa, zai girmama duk irin sakamakon zaben jin ra'ayoyin jama'a a kasar Birtaniya da za a samu. Amma ya bayyana cewa, idan kasar Birtaniya ta janye daga kungiyar EU, hakan zai kawo illa ga nahiyar Turai har ma dukkan kasashen yammacin duniya.

Kana Tusk ya bayyana cewa, idan aka nuna goyon baya ga kasar Birtaniya da ta janye daga kungiyar EU, za a sa kaimi ga wasu kasashen da suka nuna shakku ga kungiyar EU da su janye daga kungiyar. Wannan zai zama mataki na farko na wargaza kungiyar EU.

A nasa bangare, Costa ya bayyana a gun taron manema labarum cewa, kasar Birtaniya tana da muhimmanci ga kungiyar EU, yana fatan kasar Birtaniya za ta ci gaba da zama memban kungiyar EU kamar yadda kasar Portugal ta yi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China