in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya yi musayar ra'ayi da John Kerry na Amurka ta wayar tarho
2016-06-19 12:49:10 cri
A jiya Asabar, bisa gayyatar da aka yi masa, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi musayar ra'ayoyi da John Kerry, sakataren kula da harkokin wajen Amurka ta wayar tarho kan dangantakar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka, da sauran batutuwa masu alaka.

Mr. Wang Yi ya jaddada babbar ka'idar da kasar Sin take bi wajen batutuwan da suke shafar jihar Tibet, kuma ya nemi bangaren Amurka da ya daina tsoma baki kan harkokin cikin gida na kasar Sin, kuma ya dauki matakan a zo a gani wajen kare dangantakar dake kasancewa tsakanin kasashen Sin da Amurka.

A nasa bangaren, John Kerry ya bayyana cewa, bangaren Amurka bai canja manufofinsa game da yankin Tibet ba, kuma ba za a canja su ba. A ganin bangaren Amurka, yankin Tibet wani yanki ne da ba za a iya raba shi daga kasar Sin ba, bangaren Amurka ba zai nuna goyon baya ga yunkurin 'yancin Tibet ba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China