in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping da Abdel Sisi sun aikewa juna sakon taya murnar cika shekaru 60 da kafa huldar diflomasiyya tsakanin kasashen su
2016-05-30 20:56:21 cri
A 'yan kwanakin baya ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na kasar Masar Abdel Fattah al Sisi suka aike wa juna sakon taya murnar cika shekaru 60, da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin kasashen na su.

A cikin sakonsa, Xi Jinping ya ce, idan aka yi hangen nesa na nan gaba, akwai imani da kyakkyawar makomar hulda tsakanin kasashen Sin da Masar. Mr. Xi ya ce, yana fatan hada kai da Al-Sisi a kokarin zurfafa huldar abokantaka dake tsakanin kasashen biyu, bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, domin kawo alheri ga kasashen biyu, da al'ummominsu baki daya.

A nasa bangaren, Mr. Abdel Fattah al Sisi ya bayyana cewa, an daga matsayin huldar hadin gwiwa tsakanin Masar da Sin zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni, matakin da ya alamta cewa, shugabanni da kuma al'ummomin kasashen biyu suna cigaba da daukar matakai na bunkasa huldar hadin gwiwa tsakaninsu, da nufin sada al'ummun su da moriya, da kuma cimma buri na neman samun ci gaba ba tare da tangarda ba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China