in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya yi tsokaci game da aniyar jibge makamai masu linzami a yanin Koriya ta kudu
2016-02-13 12:42:34 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya yi kira ga Amurka da ta kaucewa daukar matakin jibge makamai masu linzami na tsaro, wato THAAD a kasar Koriya ta kudu, kasancewar hakan na iya zama barazana ga kasar Sin.

Mr. Wang ya bayyana hakan ne a jiya Jumma'a a birnin Munich na kasar Jamus, yayin zantawarsa da wakilin kamfanin dillancin labaru na Reuters.

Ya ce a zahiri take cewa Amurka na shawarta jibge na'urorin kakkabo makamai masu linzami a kasar Koriya ta kudu, sai dai daukar wannan matakin zai shallake bukatar tsaro a zirin na Koriya, ya kuwa shafi fadin wasu sassan yankunan nahiyar Asiya.

Ministan harkokin wajen kasar ta Sin ya kara da cewa, matakin da Amurka ke aniyar dauka, zai shafi manufofin tsaron kasar Sin, da ma na wasu sauran kasashen nahiyar, don haka Sin ke fatan dakatar da daukar sa.

Mr. Wang ya ce ko da yake ana iya bayyana wasu dalilai na zahiri game da shawarar ta Amurka, a hannu guda kowa ya san manufar hakan ta zarce wadda ake bayyanawa duniya. Hasali ma dai mataki ne da ka iya zama barazana ga tsaron kasar Sin. Don haka ya dace a dakatar da daukar sa ba tare da wani bata lokaci ba. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China