in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta magance karancin tumaturi a kasar
2016-06-15 10:27:47 cri
Karamar ministar masana'atu da zuba jari ta Najeriya Hajiya Aisha Abubakar ta ce gwamnatin kasar ta kammala wani shiri da nufin magance matsalar karancin tumatir da kasar ke fuskanta.

Ministar ta bayyana hakan ne ga manema labaru a Abuja, a lokacin taron masu ruwa da tsaki a fannin, ta ce ma'aikatar za ta kafa kwamitin kwararru a makon gobe domin su samar da wani rubutaccen tsari don tunkarar matsalar.

Ta ce asali ma, an shirya taron ne da nufin nazarin hanyoyin da za'a bi don kawo karshen matsalar karancin tumatir da kasar ke fuskanta sakamakon barkewar annobar kwari dake lalata tumatir a sassan kasar.

Aisha ta ce kwamitin kwararrun wanda zai fara aiki a makon gobe zai samar da wani tsari don daukar matakai cikin hanzari gabanin fara noman tumatir na shekara mai zuwa.

Masu ruwa da tsaki a harkar tumatir da suka hada da manoma da masu sarrafa shi da wakilan hukumomin da ma'aikatu da abin ya shafa ne suka halarci taron. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China