in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barack Obama zai yi taro kan yaki da kungiyar IS
2016-04-09 14:09:38 cri
A jiya Jumma'a, fadar shugaban kasar Amurka ta sanar da cewa, shugaba Barack Obama zai kira taron kwamitin tsaron kasa a mako mai zuwa, domin waiwaye kan irin sakamakon da aka samu cikin 'yan kwanakin da suka wuce na yaki da kungiyar IS.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, wani babban jami'in rundunar sojan Amurka da ya bukaci a sakaye sunansa, ya bayyana a farkon watan Afrilu cewa, ma'aikatar tsaron Amurka tana duba yiwuwar tura karin sojoji na musamman zuwa Syria. Amma babu wata masaniya kan hakikanin yawan sojojin da za a tura.

Manazarta sun bayyana cewa, watakila taron da za a kira a makon gobe na da alaka da wannan batu.

Shugaban manyan kwamandojin soja na Amurka, Joseph F. Dunford ya bayyana a kwanan baya cewa, zai mika wani shirin kara tura sojojin Amurka zuwa Iraki ga shugaba Obama, domin taimakawa rundunar sojan Iraki wajen fuskantar hare haren da kungiyar IS ke kaiwa birnin Mosol.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China