160616-Ghana-tayi-nasarar-zuwa-mataki-na-gaba-a-wasannin-share-fage-na-Africa-U-20-zainab.m4a
|
Da farko dai kungiyar wasa ta Young Walias na kasar Habasha ta yi nasara da ci 2 da 1 a wasan farko da aka buga a Addis Ababa.
Dan wasan tsakiya Yaw Yeboah ya zara kwallo yayin da 'yan wasan gaba Dauda Mohammed da Evans Mensah suka zara ragowar kwalleye biyu, lamarin da ya baiwa kungiyar wasan nasarar tsallakawa mataki na gaba.
Yanzu dai kungiyar wasan ta Black Satellites zata kara da takwararta ta kasar Senegal a wasan karshe na share fagen.
Za'a buga wasan farko ne a karshe mako a ranakun 8 zuwa 10 ga wata Yuli a Dakar, sannan bayan makonni biyu a buga wasa na biyu a kasar Ghana.
Kungiyoyin wasanni 7 ne zasu fafata inda za'a tantance kungiyar wasan da zata halarci wasan cin kofin Afrika na 'yan kasa da shekaru 20 wanda kasar Zambiya zata karbi bakuncinsa a ranakun 26 ga watan Fabrairu zuwa 12 ga watan Maris na shekarar 2017.(Ahmad Fagam)