in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ibrahimovic zai sanya hannu kan kwantiragin sa da Manchester United
2016-06-07 11:13:04 cri
Kungiyar kwallon kafar Manchester United ta kasar Ingila, za ta dauko dan wasan gaban kasar Sweden Zlatan Ibrahimovic, a daidai gabar da sabon kocin ta Jose Mourinho ke shirin daidaita sahun kungiyar.

Mataimakin babban jagoran kungiyar Ed Woodward ne ke jagorantar tattaunawa da wakilan Ibrahimovic, ana kuma hasashen cewa dan wasan mai shekaru 34 a duniya, zai fara takawa Man United kwallo kafin gasar kasashen turai dake tafe nan gaba cikin wannan shekara ta 2016.

A baya dai Ibrahimovic ya taka leda a kungiyoyin Malmo, da Ajax Amsterdam, da Juventus, da Inter Milan, da Barcelona da kuma AC Milan. Yanzu kuma kwantiragin sa na daf da kammala a kungiyar PSG. Ya kuma dauki kofuna tare da kungiyoyi daban daban da ya bugawa wasa, ciki hadda kofin Premier na Ingila, da kofin zakarun kulaflikan Swiden, da Serie A na Italiya, da La Liga ta Sifaniya, da kuma Ligue 1 na kasar Faransa.

A wasannin share fagen gasar nahiyar turai kuwa, Ibrahimovic ya zura kwallaye 11 cikin 19 da Sweden ta ci, wanda hakan ya baiwa kungiyar ta sa ta Sweden gurbi a gasar da za a buga a kasar Faransa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China