in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Ghana ta fara aiwatar da kashi na biyu na shirin inshorar masunta
2016-06-13 13:05:19 cri
Rahotanni daga Ghana na cewa, daga watan Yulin wannan shekara gwamnatin kasar za ta fara aiwatar da kashi na biyu na shirin ba da inshora ga masuntan kasar kimanin miliyan daya.

A saboda haka, wannan mataki na gwamnati, ministar kiwon kifi da halittun ruwa ta kasar Sherry Ayittey ta yi kira ga masuntan kasar da su hanzarta yin rajista domin amfana da wannan dama yadda ya kamata, domin magance kalubalolin da za su iya fuskanta sakamakon hadarurrukan da ke faruwa ba zato ba tsammani.

Bisa wannan shirin inshora, masunta za su sami kudi idan kayayyakin aikinsu suka lalata sakamakon hadarurruka, ko kuma idan wani ya rasu a yayin da ya ke gudanar da ayyukan da abin ya shafa ko kuma ya ji rauni har ba zai iya yin wannan sana'a ba.

Haka kuma, ko da ba su gamu da hadari ba, a karshe masunta za su sami kudin inshora da gwamnatin ta biya musu tun farko. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China