in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Ghana ya ziyarci kasar Cote d'Ivoire
2016-06-03 09:17:10 cri
Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama da takwaransa na kasar Cote d'Ivoire Alassane Outtara, sun tattauna kan wasu muhimman batutuwa da ke shafar moriyar kasashen su.

Wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta Ghana ta fitar, ta bayyana cewa, matakan magance takaddama kan iyakar ruwan kasashen biyu da kuma karfafa tsaron shiyyar, suna daga cikin batutuwan da shugabannin biyu suka tabo a lokacin ganawarsu ta ranar Laraba.

A jawabinsa shugaba Ouattara ya ce, ya yaba da rawar da takwaransa na Ghana ya taka wajen bunkasa sabon hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Shugabannin biyu sun kuma shaidawa taron manema labarai na hadin gwiwa cewa,tattaunawar tasu ta mayar da hankali kan bunkasa harkokin tattalin arziki tsakanin kasashen biyu da kuma bunkasa tsaro a shiyyar.

Shugaba Mahama ya kai ziyarar aiki ta yini biyu kasar Cote d'Ivoire ne bisa gayyatar shugaba Ouattara .

Kasashen Ghana da Cote d'Ivoire sun gabatar da kara a kotun kula da dokokin teku ta duniya dangane da batun shata kan iyaka ta ruwa tsakanain sassan biyu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China