Mahama ya tabbatar da hakan ne a lokacin da yake jawabi a bikin tunawa da kafuwar jam'iyya mai mulkin kasar shekaru 24 da suka gabata, ya ce jamiyyar ta NDC ba zata taba shiga duk wani lamari da ya shafi tada hankula ko cin zarafi ko yin batanci a lokacin gangamin yakin neman zabenta ba.
Shugaban na Ghana ya bukaci dukkannin jam'iyyun siyasar kasar wadanda zasu shiga zaben na bana dasu dauki dukkan matakan tabbatar da zaman lafiya a kasar.(Ahmad)