in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yaba da matsayar da aka cimma game da komawar Riek Machar a birnin Juba
2016-04-23 12:00:36 cri
Sakataren janar na MDD, Ban Ki-moon, ya bayyana jin dadinsa a ranar Jumma'a kan matakin da gwamnatin kasar Sudan ta Kudu ta dauka na amincewa da shawarar cimma matsaya game da sharudan da suka shafi dawowar mataimakin shugaban kasa na farko da aka zaba, Riek Machar, a Juba, babban birnin kasar.

A cikin wata sanarwa ta bakin kakakinsa, mista Ban ya nuna cewa matsayar da aka cimma an same ta ne tare da taimakon kokarin kwamitin ruwa biyu da ke sanya ido da kimantawa, har ma da abokan huldar shiyoyyi da kuma na kasa da kasa.

Shugaban MDD ya bayyana fatan ganin cewa wannan matsayar da aka cimma za ta taimakawa wajen kafa wata gwamnatin hadin kasa na wucin gadi cikin wannan kasa cikin gaggawa da kuma aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da bangarorin biyu suka rattabawa hannu a cikin watan Augustan shekarar 2015.

Haka kuma, ya yi kira ga dukkan abokan hulda na shiyoyyi da na kasa da kasa da su ci gaba da tallafawa ci gaban aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China