in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kiran baiwa matasa dama domin yin rigakafin kaifin kishin addini
2016-06-04 13:21:46 cri
A yayin wani taron manyan jami'ai kan yara da matasa da suka yi fama da kaifin kishin addini, a ranar Juma'a a cibiyar MDD dake birnin New York, manyan jami'an MDD sun yi kira da a bullo da damammaki ga matasa domin kauce su daga jan hankalin fadawa tarkon tashin hankali.

Taron wata muhimmiyar dama ce domin babban taron ya kai ga cimma wata fahimta mai kyau kan wannan batu bisa tsarin aiki na sakatare janar dake shafar yin rigakafin kaifin kishin addini da kuma a lokacin da muke nazarin dubarar baki daya kan yaki da ta'addanci dake da shekaru goma, in ji shugaban babban taron MDD, mista Mogens Lykketoft.

Yara da matasa sun yi fama ta fuskar tashin hankali kana sosai daga kaifin kishin addini a tsawon shekarun baya bayan nan, matasa sun yi fama ta fuskar mataki mataki game da bambance bambance, tauye hakki da kuma rashin aikin yi, in ji a nasa bangare mataimakin sakatare janar na MDD, Jan Eliasson, a cikin jawabinsa.

Ya tunatar da cewa asusun MDD na karfafa zaman lafiya ya kaddamar da wani shiri zuwa ga matasa. Wannan shiri na samarwa kungiyoyin matasa wani tallafin kudi domin ba su damar kafa ayyukan kansu na karfafa zaman lafiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China