Siasia wanda ya bayyana hakan bayan da kasar Denmark ta doke Dream Team din da ci 6 da biyu, a wasan da suka buga ranar Asabar, ya ce tun da yake horas da 'yan wasa ba a taba doke kungiyar sa da ci 6 ba. Dream Team na Najeriya dai sun buga wasa ne da takwarar su ta kasar Denmark a filin wasan Goyang na kasar Koriya ta Kudu, a ci gaba da buga gasar Suwon da ake yi.
Siasia ya ce 'yan wasan sa sun yi sakaci wajen tsaron gida kana 'yan wasan gaba suka kasa cin kwallaye bayan samun damammaki masu yawa. Duk dai da hakan kocin ya ce wasan da suka bugawa ya ba su damar sake duba na tsakani ga kungiyar domin zaben 'yan wasan da za su wakilci kasar a gasar Olympics dake tafe.
Kafin wasan ta da Denmark, kungiyar Dream Team ta Najeriyar ta fara da rashin nasara ne a wasan ta da koriya ta Kudu, inda Koriyan ta jefa mata kwallo daya mai ban haushi, a wasan da suka buga ranar Alhamis.(Saminu Alhassan)