in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
RD-Congo: Dubban magoyan jam'iyya mai mulki sun yi maci domin nuna goyon baya ga shugaba Joseph Kabila
2016-06-05 12:47:44 cri
Wata zanga zangar lumana ta tattara dubban magoyan bangaren masu rinjaye a ranar Asabar a birnin Kinshasa, domin kawo goyon baya ga shugaban RD-Congo da matakin kotun tsarin mulki ta dauka na baiwa Joseph Kabila damar tsayawa kan mulki har zuwa zaben sabon shugaban kasa.

Wannan maci da ya soma daga unguwar Bandal, da hadewa a filin Verodrome de Kintambo, inda sakatare janar na jam'iyyar PPRD mai mulki, Henri Mova Sakani, ya dauki magana domin nuna godiya ga magoya bayansu da suka zo da dama domin nuna goyon baya ga Joseph Kabila.

An hadu domin nunawa duniya cewa suke da babban rinjaye na al'ummar dake bayansu, dake kuma bayan shugaba Joseph Kabila, in ji Henri Mova Sakani a dandali.

A cikin jawabinsa, mista Sakani yayi allawadai da halayyar 'yan adawa, da a cewarsa, suke taro a kasashen Turai domin yin zagon kasa ga jamhuriya maimakon su dawo su koma teburin shawarwari da shugaba Kabila ya kira.

Duk abin zagon kasa da za su yi, maganar gaskiya ita ce ba za a yi zabuka a wannan shekara a RD-Congo ba, in ji Henri Mova Sakani a gaban jama'a, kafin ya kara da cewa wannan maci ya nuna babban goyon jam'iyyu da al'ummar kasa suke nunawa shugaba Joseph Kabila. Zanga zangar ta gudana cikin lumana, mako guda bayan jam'iyyun adawa sun gudanar da ta su zanga zanga domin yin allawadai da matakin kotun tsarin mulki. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China