in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sanda sun yi arangama da magoyan bayan 'yan adawa a Kinshasa
2016-05-26 21:10:58 cri
Rahotanni daga Kinshasa babban birnin Jamhuriyar demokiradiyar Congo na cewa, yau da safe 'yan sanda sun yi taho mu gama da magoyan bayan 'yan adawa da ke zanga-zanga.

Fadan dai ya barke ne lokacin da dubban masu zanga-zanga da shugabanninsu ke yi musu rakiya suka nemi tsalakawa yankin gidajen jama'a da hukumomin kasar suka killace.Inda 'yan sanda suka yi amfani da hayaki mai sa kwalla don tarwatsa masu zanga-zangar.

Magoya bayan 'yan adawar sun shirya zanga-zangar ce domin suna rashin amincewarsu da hukuncin baya-bayan da kotun tsarin mulkin kasar ta yanke na baiwa shugaba Jospeh Kabila iznin zama a kan mulki bayan karewar wa'adinsa har zuwa lokacin da za a shirya zaben shugaban kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China