in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
RD-Congo: Hukumomi sun dauki matakan rigakafi domin yaki da zazzabin shawara
2016-06-01 10:22:42 cri
Hukumomin jamhuriyar demokaradiyyar Congo (RD-Congo) sun dauki matakan rigakafi domin yaki da annobar zazzabin shawara a cikin birnin Kinshasa, a cewar wasu majiyoyi daga ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Congo a ranar Talata.

Ma'aikatar kiwon lafiya na gudanar da wani kamfe yin allura ta gama gari, da tuni aka kammala a babban birnin kasar da kuma a yanzu haka kuma ake gudanar da irin wannan kamfe a cikin sauran yankunan kasar. A cikin wata sanarwa ta kungiyar likitoci marasa kan iyakar kasa (MSF) da aka fitar a ranar Talata, mutane 48 aka tabbatar sun karbu da zazzabin na shawara tun karshen watan Febrairu a RD-Congo. Yawancin mutanen sun fito daga kasar Angola. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China