in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan adawa a DR Congo sun fara wata zanga-zanga a Kinshasa
2016-05-26 20:05:27 cri
A yau Alhamis ne magoya bayan 'yan adawa a Jamhuriyar demokiradiyar Congo suka fara wata zanga-zanga a Kinshasa,babban birnin kasar, ko da ya ke ya zuwa yanzu babu wani rahoton arangama tun faruwarta a kusa da Triomphal bouleyard.

Manufar shirya zanga-zangar, da shugabannin 'yan adawar ke yi wa dubban magoya bayan nasu jagora dauke da tutocin jam'iyyunsu, ita ce, nuna rashin amincewarsu da hukuncin da kotun tsarin mulkin kasar ta yanke na baiwa shugaba Joseph Kabila damar zama a kan mulki fiye da karshen wa'adinsa, wato har zuwa lokacin da aka shirya wani sabon zaben shugaban kasa.

A baya-bayan nan hukumar zaben kasar mai zaman kanta wadda ke da alhakin shirya zabuka a kasar ta bayyana cewa, ba za ta iya shirya zabuka a karshen wannan shekara ba kamar yadda aka tsara,domin tana bukatar watanni 17 kafin ta sake sabunta rijistar masu zabe.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China