in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an tsaron kan iyaka na Congo sun kashe 'yan sandan kasar Uganda hudu
2016-05-22 11:24:52 cri
Sojojin ruwan kasar Congo sun kashe 'yan sandan kasar Uganda hudu a yayin wani gumurzu da ya faru a ranar Asabar a tafkin Albert na gundumar Ituri dake gabashin RD-Congo.

Wani jami'in kan iyaka ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa masunta sun tabbatar shigowar 'yan sandan Uganda a cikin RD-Congo.

Wadannan 'yan sandan Uganda sun gudanar da kama jiragen ruwan kamun kifi na Congo, a cewar wannan majiya.

Zuwan rundunar sojojin ruwan Congo, ya janyo musanyar wuta tsakanin bangarorin biyu, lamarin da ya hadasa mutuwar dukkan 'yan sandan hudu da jikkatar soji daga bangaren RDC, in ji Olivier Umaka, wani jami'in ma'aikatar muhalli dake kan iyaka da tafkin Albert. An isar da gawawwakin 'yan sandan Uganda a Bunia, wani yankin dake yammacin tafkin Albert.

An dai fara tuntubar juna tsakanin hukumomin Uganda da RD-Congo, kan wannan lamari, ko da yake har yanzu kasashen biyu ba su yi wata sanarwa ba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China