in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU: Farfado da tattalin arziki da sake ginin Sudan ta Kudu na da matukar muhimmanci
2016-05-02 11:30:13 cri
Shugabar hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka AU uwargida Nkosazana Dlamini-Zuma, ta ce ya kamata a sanya batun farfado da al'amura, da sake ginin Sudan ta kudu gaban duk wani kuduri, a yayin da Sudan ta kudun ke haramar ban kwana da tashe-tashen hankula da yakin basasa.

Cikin wata sanarwar da ofishin ta ya fitar, uwargida Zuma, ta jinjinawa nadin sabbin ministocin gwamnatin rikon kwarayar kasar da shugaba Salva Kiir Mayardit ya yi, bisa tanajin yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya da aka cimma a bara. Ta ce daukar wannan mataki zai taimaka matuka wajen shawo kan matsalolin dake addabar kasar.

Zuma ta kara da cewa tashe tashen hankula da suka rika faruwa cikin kusan shekaru biyu da rabi a Sudan ta Kudu, sun haddasa gagarumin koma baya ga tattalin arzikin kasar, tare da gurgunta zamantakewa da tsarin siyasar kasar, matakin da ya kai ga fadawar al'ummar ta cikin tsananin bukatar tallafin jin kai. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China