in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xinjiang na shirin sake tsugunnar da matalauta fiye da dubu 26 dake yankunan karkara a shekarar 2016
2016-05-29 12:21:10 cri
Jihar Xinjiang mai cikin gashin kanta ta Ouigour dake arewa maso yammacin kasar Sin na shirin sake tsugunar da matalauta fiye da dubu 26 dake yankunan karkara a cikin wannan shekara, bisa darajar fiye da Yuan biliyan 1.5 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 230.

Kwamitin cigaban shiyyar da kuma yin gyare gyare na jihar Xinjiang na hasashen sake tsugunar da iyalai 7.692, da aka rarraba a cikin kauyuka 463, a cikin tsarin wani alkawarin da ya shafi taimakawa mutane dubu 200 samun sabbin gidajen zama nan da shekarar 2020.

A yayin tsawon shekaru biyar da suka gabata, mutane miliyan 1.74 dake jihar Xinjiang suka fita daga kangin talauci da kuma yawan mutane matalauta ya ragu fiye da rabi domin cimma kashi 15 cikin 100.

Jihar Xinjiang na da burin fitar da mutane miliyan 2.61 da suka yi kaura daga kangin talauci nan da shekarar 2020. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China