in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
"Yan matan kabilar Uygur sun mika kayan sassaka ga babban sakataren jam'iyyar kwaminis na kasar Sin.
2015-09-21 10:35:43 cri
A jiya Lahadi an kaddamar da bikin nune-nunen cigaban kabilar Uygur a jihar Xinjiang ta Sinn na cikar ta shekaru 60 mai taken "Rungumi kasar Sin" a nan birnin Beijing, inda aka nuna kayan sassaka da 'yan mata kabilar Uygur guda 2 suka mika wa babban sakataren jam'iyyar kwaminis ta Sin Xi Jinping.

A bangon da ke dakin nune-nune, an rataya wani kayan sassaka da ke da mita 1.52, kuma an nuna hoton shugaban Xi, da alamar tambarin jam'iyyar, da tutar kasar Sin da babban filin Tian'anmen da sauransu.

Wadan nan Kawaye guda 2 ne daga gundumar Kuqa ta yankin Aksu ta jihar Xinjiang sun yi wannan kayan sassaka ne da hannu, don yabawa babban canji da aka samu a garinsu bayan da kwamitin tsakiya ya fidda wasu kyawawan manufofi gare su.

Haka kuma, an nuna wasiku da wadannan 'yan mata suka rubuta wa babban sakataren Xi, inda aka nuna cewa, dalilin da ya sa suka iya zaman walwala, sabo da kyawawan manufofin da jam'iyyar da gwamnatin suka bayar, kuma wannan ya nuna kaunar babban sakatare Xi ga jihar Xinjiang, shi ya sa, wadannan 'yan mata sun kashe watanni 2 don sassaka wannan kaya da ke da ma'anar "Hadin gwiwa don cimma burin kasar Sin", kuma sun nuna kyakkyawar fatan su ga kasar Sin tare da godewa babban sakataren Xi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China