in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 65 sun mutu a sakamakon fashewar boma-bomai a yankunan dake dab da teku a kasar Syria
2016-05-23 20:00:35 cri
Kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya bayar da labarin cewa, wasu boma-bomai sun fashe a yankunan dake dab da teku a arewa maso yammacin kasar Syria. Kididdiga na nuna cewa, hare-haren sun haddasa mutuwar mutane a kalla 65.

Rahotanni na cewa, an kai hare-hare da boma-bomai sau uku a birnin Tartus, wadanda suka haddasa mutuwar mutane a kalla 20.

A wannan rana da safe, wasu boma-bomai sun fashe a asibiti da hukumar kula da samar da wutar lantarki da wata tashar motoci a birnin Jableh, ya zuwa yanzu hare-haren sun yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 45.

Daga bisani kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai hare-haren boma-bomai da aka kai a biranen Tartus da Jableh. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China