in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta yi kira da a tsagaita bude wuta na sa'o'i 72 a yankuna biyu na Syria
2016-05-24 10:54:47 cri
A jiya Litinin ne hukumar tsaron kasar Rasha ta yi kira da a tsagaita bude wuta har tsawon sa'o'i 72 a garin East Gouta, da kuma garin Darayya, dake yankin karkarar Damascus, fadar mulkin kasar Syria, tun daga yau Talata.

A kuma wannan rana, shugaban cibiyar dake kula da aikin warware ricikin Syria ta kasar Rasha dake kasar Syria Sergey Kuralenko, ya bayyana cewa, kiran da mahukuntan Rasha suka yi domin ganin an shimfida yanayin kwanciyar hankali a kasar Syria, ya sa hukumar tsaron kasa yin kira ga bangarori daban daban da abin ya shafa, da su dakatar da musayar wuta tsakaninsu, su kuma kawar da alaka da kungiyar ta'addanci ta Jabhatal-Nusra, duba da cewa sojojin kasar ta Rasha za su ci gaba da kai hari ta sama, kan yankunan dake karkashin ikon 'yan ta'addan. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China