in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU tayi Allah wadai da hallaka hafsan sojin Burundi
2016-04-27 11:04:02 cri
Kungiyar tarayyar Afrika AU ta yi Allah wadai da kashe birgediya janar Athanase Kararuza, babban mai bada shawara kan harkokin tsaro a ofishin mataimakin shugaban kasar Burundi.

Nkosazana Dlamini-Zuma, shugabar AU, ta yi tur da hallaka jami'in cikin wata sanarwar da AU ta fitar a ranar Talatar data gabata.

Marigayi birgediya janar Kararuza, shi ne tsohon mataimakin babban kwamandan tawagar wanzar da zaman lafiya a jamhuriya tsakaiyar Afrika CAR (MISCA), kuma jami'in kwamitin wanzar da zaman lafiya na MDD a CAR (MINUSCA).

Sanarwar ta ce, mai dakin marigayi birgediya janar Kararuza ma ta rasa ranta a lokacin harin, sannan wata 'yar sa ta samu munanan raunuka.

Dlamini-Zuma, ta aike da sakon ta'aziyya a madadin AU ga iyalan marigayin tare da yin fatar samu sauki ga diyar tasa.

Madam Dlamini-Zuma, ta ce ana ta fuskantar munanan hare hare a 'yan kwanakin nan, kuma akwai alamun rikicin zai iya bazuwa zuwa ga sassan kasar ta Burundi har ma da kewayen kasar.

AU ta bayyana hare haren a matsayin cin zarafi ga rayuwar bil adama sannan ta bukaci a gudanar da bincike domin gano wadanda keda hannu don hukunta su. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China