in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An damke mutune 4 bisa zarginsu da hannu a kashe hafsan soji a Burundi
2016-04-30 13:30:41 cri
Mutane 4 ne aka kama bisa zarginsu da hannu wajen kashe babban hafsan rundunar sojin kasar Burundi a farkon wannan mako.

Babban mai shari'a na kasar Valentin Bagorikunda, ya fada a Juma'ar data gabata cewa, ana cigaba da gudanar da bincike domin gano sauran mutanen da ake zarginsu da hannun a wannan danyen aiki.

Marigayi birgediya janar Athanase Kararuza, shi ne babban mai bada shawara ta fuskar tsaro a ofishin mataimakin shugaban kasar, kuma an harbe shi ne a daidai lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa wajen aiki da safiyar ranar Litinin a babbban birnin kasar Bujumbura.

Kuma a lokacin yana cikin motarsa inda aka hallaka shi tare da matarsa da mai tsaron lafiyarsa nan take, sannan 'yarsa ta samu munanan raunukuna a lokacin harin, sai dai ita ma daga bisani ta rasu a ranar Alhamis din data gabata.

Bagorikunda ya ce, ana cigaba da shari'a ga wasu da ake zargi da kashe wasu manyan jami'an sojojin kasar a 'yan watannin da suka gabata.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China