in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burundi ta karyata batun shirya shawarwari a cikin watan Mayu a Arusha
2016-04-27 11:17:51 cri
Gwamnatin kasar Burundi ta karyata a ranar Talata wasu labaran da ke yaduwa a kan shafukan yanar gizo ko kuma kan kafofin watsa labaru na kasashen duniya kan batun shirya shawarwari tsakanin gwamnati da dukkan masu ruwa da tsaki a fagen siyasar kasar Burundi daga ranar 2 zuwa 6 ga watan Mayu a birnin Arusha na kasar Tanzaniya.

Mista Willy Nyamitwe, babban mai bada shawara na fadar shugaban kasar Burundi, da ke kula da harkokin sadarwa, ya jaddada cewa wadanda suka salwantar da rayuwar 'yan kasa, da kuma suka nemi kifar da hukumomin kasa da aka zabe su ta hanyar demokaradiyya da sauransu da suka shiga tawaye da makamai a cikin kasar ba za a iya gayyatarsu ba a cikin wannan tattaunawa ta tsakanin 'yan kasar Burundi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China