Game da hakan, sakatare janar na M.D.D. Ban Ki-Moon ya fidda wata sanarwa, inda ya yi Allah-wadai da lamarin, kuma ya yi kira da a gabatar da wadanda suka aikata wannan ta'asa gaban kuliya.
Sanarwar ta ce bisa kwarya-kwaryar labarin da aka samu, an ce an kai harin bom ga ayarin motoci na sojojin samar da zaman lafiya ta M.D.D. da ke kasar Mali, a wani wuri da ke da nisan kilomita 15, a arewa da birnin Aguelhok da ke yankin Kidal, harin da kuma ya hallaka sojoji 'yan asalin Chadi 5.(Bako)