in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai harin boma-bomai a birnin Kameshli na kasar Syria
2016-05-15 12:58:26 cri
A jiya Asabar 14 ga wata, gidan talebijin na kasar Syria ya ba da labarin cewa, an kai harin boma-bomai da aka dasa cikin mota kan birnin Kameshli dake arewa maso gabashin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 5 a wannan rana.

An kai harin ne a wata tashar bincike ta rundunar sojan kiyaye jama'ar kurdawa dake birnin Kameshli. Kamfanin dillancin labaru na Syria ya ba da labari dangane da haka, amma kawo yanzu ba a san kowane ne ya kai wannan hari ba.

Yawan kurdawa ya kai kashi daya bisa goma na yawan mutanen Syria, yawancinsu suna zama a yankin iyakar kasa tsakanin arewacin Syria da Iraki da kuma Tukiyya, kuma birnin Kameshli da aka kai hari a wannan karo matsugunin kurdawa ne.

A wannan rana kuma, an kai harin boma bomai da aka dasa cikin mota a jihar Deir ez-Zor dake gabashin kasar, amma ya zuwa yanzu babu wata masaniya kan yawan mutanen da suka mutu ko jikkata ba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China