in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ce watakila jirgin saman kamfanin Masar ya fadi
2016-05-20 11:23:29 cri
A jiya Alhamis ne, wani jirgin sama na kamfanin zirga-zirgar jiragen saman kasar Masar wanda ya tashi daga birnin Paris na kasar Faransa zuwa Alkahira na kasar Masar ya bace a yankin tekun Bahar Rum. Ministan harkokin zirga-zirgar jiragen sama na kasar Masar Sherif Fathy ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar kan batun bacewar jirgin sama mai lamba MS804 na Masar a wani ginin dake dab da filin jiragen saman birnin Alkahira a yammacin jiya cewa, yanzu ana gudanar da bincike don gano musabbabin bacewar jirgin saman. Koda yake mai yiwuwa ne jirgin saman ya fadi, amma kafin a gano tarkacen jirgin saman, yana da kyau a yi amfani da kalmar 'bace' maimakon 'fadi'.

A nasa bangare, shugaban kasar Faransa François Hollande ya bayyana a tsakar ranar 19 ga watan a birnin Paris cewa, yanzu ba a tabbatar da dalilin faruwar hadarin ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China