in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta gurfanar da wasu masu fafutuka da kisan wani babban alkali
2016-05-09 13:46:57 cri
Jiya Lahadi, ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Masar ta tuhumi wasu masu fafutuka na kungiyar 'yan uwa musulmi 67, kungiyar da aka rusa, da hannunsu kan kisan wani babban alkalin Masar a shekarar da ta gabata, in ji kamfanin dillancin kasar Masar MENA.

Babban alkalin Masar, Hisham Barakat, ya mutu a yayin wani harin bam da aka dana ga mota a cikin watan Junin shekarar 2015. Boma boman an sarrafa su daga nesa a lokacin tawagar motocinsa take wucewa, tare da kuma jikkata masu tsaron lafiyarsa da dama.

A cewar binciken da jami'an tsaron cikin gida na Masar suka gudanar, wadanda ake zargin akwai yiyuwar sun samu tuntubar Hamas, kungiyar Falesdinu dake da cibiya a zirin Gaza. Tare da wasu manyan mambobin kungiyar 'yan uwa musulmi, sun shirya musammun ma kai hari kan manyan jami'an gwamnati, da nufin janyo baraka da hargitsi cikin kasa.

Tuhumar ta bayyana cewa wadanda ake zargin sun samu horo a sansanonin soja na Hamas dake zirin Gaza mai makwabtaka, inda kuma suka samu boma boman da suka yi amfani da su wajen kai harin.

Kungiyar Hamas ta karyata sau da dama zargin cewa tana da hannu kan kisan Hisham Barakat, tare da tura wata tawaga a birnin Alkahira domin yunkurin maido da hulda tare da Masar, musammun ma ta hanyar fitar da sanarwowin sasantawa.

Mista Barakat ya gurfanar da miliyoyin magoya bayan tsohon shugaban kasa Mohamed Morsi, wanda ya fito daga kungiyar 'yan uwa musulmi, bisa dalilan janyo tashe tashen hankali da ta'addanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China