in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS ta dauki alhakin kai hare-hare kan 'yan sanda a kasar Masar
2016-05-09 10:15:59 cri
A ranar 8 ga wata, reshen kungiyar IS dake kasar Masar sun sanar da kai hare-hare kan 'yan sanda a kusa da birnin Alkahira babban birnin kasar Masar.

Bisa labarin da kafofin yada labaru na wurin suka bayar, an ce, a ranar 8 ga wata, dakarun dauke da makamai 4 sun kai hari ga wata motar 'yan sanda da ke garin Helwan da ke kudancin birnin Alkahira, inda suka harbe 'yan sanda 8 da ke cikin motar har lahira.

Ma'aikatar dake kula da harkokin cikin gida na kasar Masar ta sanar da cewa, a cikin wadanda suka mutu, akwai laftana guda da 'yan sanda guda 7, kuma suna cikin aikin sintiri a yankin kudancin birnin Alkahira a lokacin da lamarin ya faru.

Tun daga shekarar 2013, yankin zirin Sinai yana ta fama da tashe tashen hankali, inda dakarun dauke da makamai suke kai hare-hare ga 'yan sandan wurin, lamarin da zuwa yanzu ya yi sanadiyyar mutuwar darurruwan mutane.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China