in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karamin ministan mai a Najerriya ya yi Allah-wadai da masu fasa bututun mai a kasar
2016-05-17 10:10:35 cri
Karamin minsitan albarkatun mai na Najeriya Ibe Kachikwu ya yi Allah-wadai da yadda masu fasa batutan mai a yankin niger Delta ke yi wa aikin hako danyen mai a kasar zagon kasa.

Ibe Kachikwu wanda ya bayyana hakan a zauren majalisar wakilan kasar. Ya ce, aika-aikar tsagerun Niger Delta ta sa adadin man da kasar ta ke hakowa ta yi kasa daga ganga miliyan 2.2 zuwa ganga miliyan 1.4 a kowa ce rana.

Don haka ya bayyana kudurin ma'aikatarsa na ganin an gyara kayayyakin da aka lalata an kuma kare su yadda ya kamata.

Ministan ya kuma nanata bukatar gina kayayyakin more rayuwar jama'a, wadanda ya bayyana a matsayin ginshikin kara adadin danyen man da ake hakowa.

Rahotanni na nuna cewa, yau kusan shekaru 35 ke nan rabon a canja bututan man kasar, sannan matatun man na dab da tsayawa saboda tsufa.

Matasan da ke fasa bututan man a yankin Niger Delta dai na cewa, suna yin hakan ne saboda ba sa amfana daga kamfanoni da gwamnatin Najeriyar da ke hako albarkatun man da ke yankin nasu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China