in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban MEND ya nisanta kansa daga sabuwar kungiyar NDA
2016-05-17 09:56:50 cri
A wani labarin kuma tsohon shugaban kungiyar 'yan tawayen kwatar yankin Niger Delta (MEND) Ekpemupolo ya ce ba shi da hannu wajen kafa sabuwar kungiyar tsagerun yankin Niger Delta wato Niger Delta Avengers (NDA).

Ekpemupolo wanda aka fi sani da Tompolo ya tabbatar da hakan ne a jiya Litinin. Yana mai cewa, bai ji dadin yadda sojojin kasar suka ki yarda da kalaman nasa ba, duba da yadda 'yan tawayen na Avengers ke lalata batutan mai da ke yankin.

Don haka ya bukaci gwamnati da ta kaddamar da bincike don gano hakikanin wadanda suke da hannu wajen kafa sabuwar kungiyar tsagerun na yankin Niger Delta.

Bayanai na nuna cewa, sama da matasa 8,000 a yankin suka mika makamansu ga gwamnatin Najeriyar, a kokarin da ake yi na kawo karshen tashin hankalin da aka kwashe shekaru ana tafbakawa a yankin mai arzikin man fetur.

Tun daga shekarar 2006 zuwa wannan lokaci, sama da 'yan kasashen waje 300 da ke aikin hako mai a yankin aka sace. Ko da ya ke an saki galibinsu bayan da aka biya kudin fansa.

Fasa batutan mai a yankin a 'yan shekarun nan, ya tilastawa Najeriyar rage kusan humusi na adadin man da take hakowa. Lamarin da ya sa mahukuntan kasar tura sojoji da masu gadin gabar teku don yakar wadannan bata gari. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China