in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kira ga mahukuntan Najeriya da su magance matsalar 'yan tawaye a yankin Niger Delta
2016-05-16 09:08:16 cri

Kungiyar manyan ma'aikatan man fetur da iskar gas a Njaeriya (PENGASSAN) ta yi kira ga gwamnatin tarayyar Najeriya, da ta kawo karshen ayyukan 'yan tawaye da fasa batutan mai da ke faruwa a yankin Niger Delta mai arzikin mai.

Shugaban kungiyar Francis Olabode-Johnson wanda ya yi wannan kiran jiya Lahadi a garin Kalaba da ke kudancin kasar, ya ce akwai bukatar gwamnatin kasar Najeriya ta kara zage damtse a yakin da take yi da masu fasa batutan man da satar mai a yankin duba da yadda lamarin ke kara kamari.

Ya ce, gwamnatin kasar Najeriya tana asarar dimbin kudaden shiga sakamako yadda 'yan tawayen ke ci gaba da fasa batutan man. A saboda haka, akwai bukatar mahukuntan kasar da manyan kamfanonin da ke aikin hako mai a yankin, su yi amfani da fasahohi na zamani wajen sa-ido kan batutan man da yadda ake satar danyen man.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China