Mahalarta taron suna ganin cewa, a cikin 'yan shekarun da suka gabata, kasa da kasa sun sami ci gaba a fannin yaki da kungiyar Boko Haram, amma kamata ya yi su ci gaba da kokari, da zummar kawar da wannan kungiya baki daya.
Shugaban Faransa, François Hollande ya bayyana a gun taron kolin cewa, kungiyar Boko Haram na daya daga cikin kungiyoyin duniya da suka fi yin barazana ga bil'adam, wadda ke da alaka da kungiyar IS. Yin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a fannin yaki da ita na da muhimmanci kwarai da gaske.
A nasa bangare, ministan harkokin wajen Birtaniya, Philip Hammond ya furta cewa, ban da daukar matakan soja, kamata ya yi kasashen duniya su kara kokarinsu a fannin yaki da kungiyar Boko Haram. A wannan rana, ma'aikatar harkokin waje ta Birtaniya ta ba da sanarwar cewa, kasar za ta bayar da kudin agaji Pound miliyan 40 ga Nijeriya a cikin shekaru hudu masu zuwa, domin yaki da kungiyar Boko Haram, cikin har da kudin horar da sojojin Nijeriya 1000 domin shiga aikin soja a yankin arewa maso gabashin kasar Nijeriya.
A ranar Jumma'a 13 ga wata, kwamitin sulhun MDD ya ba da sanarwar yin Allah wadai da kai harin ta'addanci da ma sauran danyun ayyukan da kungiyar Boko Haram ta yi a yankin tabkin Chadi, kuma ya kalubalanci sojojin kasa da kasa a wurin domin kara karfin yaki da kungiyar Boko Haram yadda ya kamata.(Fatima)