in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta kuduri aniyyar kawar da cututtukan da ake samu a wurare masu zafi nan da shekarar 2020
2016-05-13 15:24:44 cri
Ministan kiwon lafiya na Najeriya, Isaac Adewole. Ya bayyana cewa,gwamnatin Najeriya ta lashi takobin kawar da cututtukan da ake samu a wurare masu zafi da ba a maida hankali kansu (MTN) nan da karshen shekarar 2020 kamar yadda da kungiyar kiwon lafiya ta duniya WHO ta tsaida a dukkan fadin duniya,

Mista Adewole ya shaidawa manema labarai haka ne a birnin Abuja, hedkwatar Najeriya,yana mai cewa gwamnati ta bullo da wani shiri mai inganci da za a aiwatar na tsawon shekara guda don ganin an kawar da wadannan cututtuka a Najeriya.

A cewar WHO, wadannan cututtukan suna yaduwa ne ta hanyoyi daban daban da ake samu a yankuna masu zafi kimanin 149 kuma suna shafar mutane fiye da biliyan guda, don haka lamari ne mai cikin kudi sosai ga kasashe masu tasowa na miliyoyin dalar Amurka a wannan shekara.

Cututtukan da ake samu a wurare masu zafi wato MTN da kungiyar WHO ta bayyana sun hada da basir din Buruli, tsutsar ciki, kuturta, ciwon gwiwa, kurkunu, cutar haukan kare, dundumi da dai sauransu kuma suna yaduwa a cikin kasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China