in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na shugaban Sin ta halarci bikin rantsar da shugaban Uganda
2016-05-14 13:16:16 cri
Jiya Jumma'a 13 ga wata, shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Sin, kana mataimakiyar shugaban zaunannan kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar ta Sin Yan Junqi a fadar shugaban kasar dake Kampala, babban birnin kasar Uganda. Haka kuma, Yan Junqi ta halarci bikin rantsar da shugaban kasar Uganda da aka yi a ran 12 ga wata.

A yayin ganawarsu, Yan Junqi ta bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan kasar Uganda wajen neman hanyar raya kasa da kanta, domin bunkasa tattalin arzikin kasar, yayin da kuma ake kyautata zaman rayuwar al'ummomin kasar, haka kuma, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa da kasar Uganda wajen aiwatar da batutuwan da shugabannin kasashen biyu suka cimma ra'ayi daya wajen yin hadin gwiwa, ta yadda za a iya kyautata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu har zuwa wani sabon matsayi.

A nasa bangaren kuma, shugaba Museveni ya ce, kasarsa tana son karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin, musamman ma a fannin habaka ayyukan masana'antu da ayyukan noma da dai sauransu, domin ba da tallafi da al'ummomin kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China