in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta bukaci Amurka da kada ta sake shakkun sakamakon zabe
2016-04-08 10:33:01 cri
Gwamnatin kasar Uganda ta bukaci a ranar Alhamis ga jakadan kasar Amurka da kada ya sake kawo shakku game da nasarar shugaba Yoweri Museveni a zaben watan Febrairun da ya gabata. Kakakin gwamnatin kasar, mista Ofwono Opondo, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Alhamis cewa jakadan Amurka madam Deborah Malac na cigaba da jaddada korafe korafenta kan kurakurai a lokacin zaben shugaban kasa. Haka kuma, ya bayyana cewa wasu tsirarrun kungiyoyi a Amurka da Turai, da ma wasu jami'an diplomasiya a kasar Uganda, na cigaba da zuba kudade ga mutanen 'yan adawa bisa manufar janyo wani canjin ta gwamnatin da ba ta sahihanci. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China