in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda zata yi hadin gwiwa da Sin a fannin sadarwa
2016-04-07 11:10:04 cri
Kamfanin Huawei na kasar Sin dake kasar Uganda ya daddale takardar fahimtar juna ta hadin gwiwa tare da ma'aikatar harkokin sadarwa ta Uganda a ranar 5 ga wata, don kara hadin gwiwarsu a fannin sadarwa. Ministan harkokin sadarwa na Uganda John Nwoono Nasasira ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Uganda tana fatan za a kara yin hadin gwiwar a fasahohin sadarwa tare da kasar Sin.

A wannan rana, an bude bikin nuna fasahohin kamfanin Huawei a birnin Kampala babban birnin kasar Uganda, inda ministan ya bayyana cewa, a shekarun baya baya nan, Sin da Uganda sun samu nasara kan hadin gwiwar a fannin sadarwa. Ana gudanar da aikin hada yanar gizo a kasar Uganda wanda gwamnatin kasar Sin ta samar da rancen kudi kuma kamfanin Huawei na Sin dake kasar Uganda ya dauki nauyin gudanarwa don cimma burin kafa yanar gizo a babban birnin kasar da manyan yankunan kasar, aikin da yanzu ya kai ga mataki na uku. Bayan da aka gama aikin, za a sa kaimi ga yin mu'amala a tsakanin hukumomin gwamnatin kasar Uganda, da kananan hukumomin gwamnatin kasar, da kyautata ayyukan gwamnatin kasar ta fannin bautawa jama'a da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China