in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Temitope ya koma buga kwallon Kwando a Uganda
2016-05-11 16:39:11 cri
Tsohon dan wasan Kwando dake buga wasa a Najeriya Ahmed Temitope, zai fara buga wasa a kungiyar Pemba Warriors ta kasar Uganda. Manajan kungiyar ta Pemba warriors Brian Gumisiriza ne ya bayyana hakan, yayin zantawar sa da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua.

Gumisiriza ya ce suna sa ran isar Temitope kungiyar nan gaba kada, matakin da zai taimakawa 'yan wasan ta samun karin gogewa, daga irin kwarewar da dan wasan ke da ita, musamman a gabar da kulaf din ke fatan daukar kofin gasar zakarun kasar na bana.

A nasa bangare Temitope, wanda a baya ya bugawa kungiyoyin kasashen Indonesia, da Thailand da Malaysia wasa, ya alkawarta baiwa sabuwar kungiyar ta sa cikakkiyar gudummawar da ta dace.

A wani ci gaban kuma, kungiyar mata ta kwallon Kwando a Najeriya na shirin shiga jerin 'yan wasan kasashe daban daban, wanda za su buga gasar Olympics ta birnin Rio. Yanzu dai haka kungiyar mai suna Tigress za ta buga wasannin share fagen gasar ta Rio da za a buga a kasar Faransa, tsakanin ranekun 13 zuwa 19 ga watan Yuni mai zuwa.

Kungiyar 'yan matan dai na cikin rukuni na C, za kuma ta fafata da kasashen Koriya ta kudu, da Belarus a birnin Nantes na kasar ta Faransa.

Da take karin haske game da shirin kungiyar Helen Ogunjimi, ta ce 'yan wasan na Najeriya za su yi duk mai yiwuwa, wajen samun gurbi a gasar ta Olympics.

Ita ma Sarah Ogoke, wadda daya ce daga taurarin 'yan wasan na Najeriya, ta ce za su yi iyakacin kokarin samarwa Najeriya nasara, a wasannin share fage da kuma gasar ta birnin Rio.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China