in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta fara shirin fuskantar gasannin AAG da na Afrobasket
2015-05-07 10:44:42 cri
Mahukuntan hukumar gudanarwar kwallon kwando a Najeriya, sun bayyana shirin su na bude atisaye, tun daga ranar Lahadi mai zuwa, domin tunkarar wasannin nahiyar Afirka da ake gudanarwa tun bayan shekaru 4, wato "All-Africa Games" a turance, da kuma gasar kwallon Kwando ta bana, ta kulaflikan nahiyar ko "Afrobasket competition".

A cewar shugaban hukumar ta NBBF Tijani Umar, kulaflikan kwallon Kwando na maza da na mata, za su fara atisaye a birnin Abuja fadar mulkin kasar, inda ake sa ran 'yan wasan kasar dake gida da na waje, zasu hallara domin gwada kwarewar su, gabanin fidda wadanda za su wakilci kasar a gasannin biyu.

Cikin tsare-tsaren da mahukuntan NBBF suka bayyana, hadda gudanar da wasannin share fage na sada zumunta, tsakanin Najeriya da wasu kulaflikan dake nahiyar Turai da kuma kasar Sin. Kana za su gudanar da ran-gadin samun horo a Amurka, kafin ranar 30 ga watan Mayun da muke ciki, lokacin da kulaf din mata na kasar zai fara buga wasannin a gasar Afrobasket, a birnin Abidjan, fadar mulkin kasar Cote D'Ivoire.

Za kuma a gudanar da gasar All-Africa Games karo na 11 a birnin Brazzaville na kasar Congo, tsakanin ranekun 4 zuwa 19 ga watan Satumbar bana.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China