in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista a Najeriya ya kauracewa shafukan facebook da twitter
2016-05-07 12:00:45 cri
Karamin ministan zirga-zirgar jiragen sama na Najeriya Hadi Sirika, ya fada a jiya Juma'a cewar ya dakatar da yin amfani da shafukansa na facebook da twitter da ma sauran shafukan sada zumunta kacokam.

Sirika, ya tabbatar da hakan ne a lokacin taron manema labaru a Abuja, babban birnin kasar, sannan ya gargadi al'umma da su yi hattara don gudun fadawa hannun bata gari wadanda ke amfani da sunansa domin damfarar jama'a ta hanyar shafukan sada zumunta.

Ministan ya ce sama da shafukan facebook da na twitter 20 ne aka bude da sunansa da hotunnasa, har ma ana amfani da shafukan wajen sanar da cewar yana raba Babura da wasu kayayyakin inda ya ce sam bashi da masaniya a kai.

Ya ce yana tabbatarwa duniya cewa ya kauraewa shafukan facebook da twitter da ma sauran shafukan sada zumunta, sannan ya musanta ikirarin da wasu ke bazawa cewa yana raba ayyukan yi ta hanyar internet.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China